in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Bahrain da Masar da Tarayyar kasashen Larabawa da Saudiya sun yanke huldar diflomasiyya da kasar Qatar
2017-06-05 11:34:32 cri
A yau ne, kasashen Bahrain da Masar da Tarayyar kasashen Larabawa da kasar Saudiya suka bayar da sanarwar yanke huldar diflomasiyya dake tsakaninsu da kasar Qatar. A cewar wadannan kasashen hudu, kasar Qatar tana goyon bayan ayyukan ta'addanci ko tana gurgunta yanayin tsaron a yankin da suke ciki.

A cikin sanarwar da ta fitar, gwamnatin kasar Bahrain ta ce, kasar Qatar tana tsoma baki a harkokin cikin gidan kasar Bahrain, baya ga goyon bayan ayyukan ta'addanci. Sakamakon haka, kasar Bahrain ta tsai da kudurin yanke huldar diflomasiyya dake tsakaninta da kasar Qatar, kana ta dawo da ma'aikantan diflomasiyyar dake kasar Qatar, Sannan ta umarci ma'aikatan diflomasiyya na kasar Qatar dake kasar Bahrain da su kwashe ya nasu ya nasu su bar kasar cikin sa'o'i 48. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China