in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Sin: manyan kasashe na da nauyin kara bada gudunmuwa wajen ciyar da al'umomi gaba
2017-02-18 17:29:21 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya yi kira ga kasashe a fadin duniya su hada kai tare da daukan matakai da suka dace.

Wang wanda ya bayyana haka a jawabinsa yayin babban taro kan tsaro karo na 53 da aka fara jiya Jumma'a a birnin Munich, ya ce muhimman batutuwan da taron ya ba muhimmanci sun hada da tattauna muhimman batutuwa kan tsaro, ciki har da kawancen kasashen yankin tekun Atlantika da dangantakar kasashen Yamma.

Ministan ya ce har yanzu, tabbatar da tsaro da samar da ci gaba, su ne muhimman batutuwa da aka sanya gaba a duniya.

Har ila yau, Wang Yi ya ce manyan kasashe na da dimbin arziki da damarmaki, don haka, suna da muhimmiyar rawar takawa wajen tabbatar da tsaro da wanzar da zaman lafiya a duniya tare da bada gudunmuwa ga ciyar da al'umma gaba. ( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China