in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Sin ya yi kira da samar da hadin kai tsakanin kasashe
2017-02-18 12:27:48 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi kira ga kasashe a fadin duniya su hada kai tare da daukan matakai da suka dace.

Wang Yi ya bayyana haka ne a jawabinsa, yayin babban taro kan tsaro da aka fara jiya Jumma'a a birnin Munich.

Yayin taron za a tattauna muhimman batutuwa kan tsaro, ciki har da kawancen kasashen yankin tekun Atlantika da dangantakar kasashen Yamma.

Ministan ya ce, cikin wasu muhimman jawabai biyu da ya yi a Switzerland cikin watan da ya gabata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi kira da gina al'ummu ta yadda za a samu ci gaba da makoma mai kyau na bai daya.

Ya ce tabbatar da tsaro da samar da ci gaba, su ne muhimman batutuwa da aka sanya gaba a duniya.

Har ila yau, Wang Yi ya ce bai kamata hadin gwiwa tsakanin bangarori da dama ya zama tsohon batu ba, a don haka ya kamata a inganta shi tare da sake karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashe. ( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China