in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Trump ya yi alkawarin nada jakadan da zai karfafa dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka
2017-05-03 09:33:29 cri
Shugaban Amurka Donald Trump ya zabi Terry Branstad a matsayin wanda zai zama jakadan Amurka a kasar Sin, har ma ya bayyana cewa idan nadin mista Branstad ya tabbata, zai yi aiki wajen samar da babban tasiri game da karfafa dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka.

A lokacin da majalisar Amurka ke yin zama don tantance shi, Branstad ya ce, a matsayinsa na gwamnan jihar Iowa yana ganin alamu na samun kyakkyawar dangantakar kasuwanci tsakanin kasashen biyu.

Ya ce idan har aka tabbatar da shi a wannan mukami, zai yi aiki tukuru wajen samar da kyakkyawan tasiri na karfafa dangantaka tsakanin Amurka da Sin.

Branstad ya fadawa 'yan majalisar Amurka cewa bangaren harkokin sufurin jiragen sama, da samar da kayayyaki a masana'antu, da sinadarai, da na'urorin lantarki, da sauran kayayyaki da ayyuka na musamman ne ake fitar da su zuwa kasar Sin a kowace rana wadanda suke matukar tallafawa ci gaban tattalin arzikin Amurka.

Sannan ya bayyana dangantakar dake tsakanin Amurka da Sin da cewa dangantaka ce ta fuskoki da dama, Branstad ya kuma lura cewa dole ne kasashen biyu su yi aiki tare wajen muhimman ayyuka da suka shafi batun tsaro, ciki har da batun dakile shirin kera makaman nukiliyar Korea ta arewa da kuma tabbatar da tsaro wajen yaki da masu yin kutse ta hanyar yanar gizo.

Branstad ya kara da cewa, zai yi kokari matuka wajen ci gaba da wanzuwar musayar al'adu da fasahohi da al'ummar Sinawa. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China