in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana fatan dangantaka tsakanin Sin da Amurka zamanin Trump za ta ci gaba, in ji jakadan Sin a Amurka
2017-01-25 18:44:29 cri
Jakadan kasar Sin da ke Amurka Cui Tiankai ya bayyana cewa, ana fata dangantaka tsakanin kasashen Sin da Amurka za ta ci gaba kamar yadda ake fata a lokacin da Donald Trump yake shugabancin kasar Amurka.

Jakada Cui wanda ya bayyana hakan a jiya Talata, ya ce ko da har yanzu Trump bai yi magana game da manufar gwamnatinsa a kan kasar Sin ba, da alamun dangantakar kasashen biyu kamar yadda aka saba ba za ta canja ba.

Jami'in na kasar Sin ya kara da cewa, dangantakar kasashen biyu ta dace da moriyarsu, kasancewarsu manyan kasashen masu karfin tattalin arziki a duniya, kana kasashe masu kujerun dindindin a kwamitin sulhu na MDD.

Ya kuma bayyana fatan cewa, bangarorin biyu za su ci gaba da rumgumar matakan tattaunawa da yin musaya kamar yadda suka saba yi a shekarun baya.

Cui Tiankai ya ce matakan da kasashen biyu suka dauka na gina sabuwar dangantakar abokantaka ta rashin takalar juna da mutunta juna da hadin gwiwar moriyar juna sun kai ga cimma gagarumar nasara. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China