in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta ba da gudunmawar sama da ton 12,000 na shinkafa ga kasar Zimbabwe
2017-04-04 12:49:24 cri
Kasar Sin ta ba da gudunmuwar Ton 12,173 na shinkafa ga kasar Zimbabwe, domin taimakawa mutanen da ke fama da fari da ya addabi kasar tun a bara.

Ministar kwadago da walwalar jama'a ta Zimbabwe Prisca Mupfumira, ta ce za kuma a raba gudunmuwar da kasar ta samu bayan neman taimakon kasashen duniya da ta yi a shekarar 2016, ga iyalan da ambaliyar ruwa ta shafa a watan Fabrairun bana.

Da take jawabi a ofishin jakadancin Sin dake Zimbabwe, Mupfumira ta ce ana sa ran shinkafar za ta isa kasar cikin watan Yuni mai zuwa.

Bayan neman gudunmuwar a shekarar 2016, Kasar Sin ta ba Zimbabwe gudunmuwar ton 19,000 na shinkafa, inda aka raba ga mabukata a fadin kasar.

Wannan na zuwa ne bayan Sin ta mika gudunmuwar dalar Amurka miliyan 1 ga kasar a ranar 31 ga watan Maris, domin taimakawa mutanen da ambaliya ta shafa a kudancin kasar.

Mupfumira ta kara da cewa gwamnatin Zimbabwe ta raba ton 481,073 na masara ga mabukata a cikin watan Oktoban bara.

Ruwa da aka yi kamar da bakin kwarya da guguwa a kasar cikin watan Fabrairu, ya yi sanadin rayukan mutane 271, yayin da ya raunata wasu 128 tare da raba kusan mutane 2,000 da matsugunansu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China