in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masar ta bukaci a warware rikicin Libya ta hanyar siyasa
2017-05-14 12:05:31 cri
Shugaban kasar Masar Abdel Fattah al-Sisi ya nanata aniyar amfani da hanyoyi na siyasa wajen warware rikcin kasar Libya.

Sisi ya fadi hakan ne a yayin tattaunawa da babban kwamandan rundunar sojin Libya Khalifa Haftar cewa, kasar Masar tana kara nuna goyon bayan cigaba da tattaunawa tsakanin bangarorin kasar ta Libya da basa ga maciji da juna domin samun maslaha don farfadowar zaman lafiya da hadin kan kasar.

Shugaban na Masar ya nanata muhimmancin tabbatar da hadin kai tsakanin dakarun kasar, kana ya nuna bukatar dage takunkumin shigo da makamai da aka azawa kasar, al Sisi ya ce dole ne a dakile hanyoyin samun kudade da na makamai tsakanin kungiyoyin yan ta'adda a kasar.

Da yake karin haske game da al'amurran tsaro a kan iyakar kasar ta yammaci wanda ke makwabtaka da Masar ya ce, kasar na cigaba da gudanar da tarukan tattaunawa a yan watannin da suka gabata domin lalibo bakin zaren magance rikicin siyasa da ya daidaita kasar ta Libya. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China