in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya: Jihar Borno ta kwashe 'yan gudun hijira 3,682
2017-05-25 09:21:12 cri
Gwamnan jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya Kashim Shettima, ya ce gwamnati ta kwashe 'yan gudun hijira 3,600 daga cikin 78,000, da suka tsere zuwa makociyar kasar Kamaru, a lokacin da ayyukan kungiyar Boko Haram suka tsananta.

Da yake jawabi a birnin Maiduguri, lokacin da yake karbar gudunmuwar kayayyakin gini da abinci daga hukumar kula da 'yan gudun hijira da 'yan ci rani ta kasar, Kashim Shettima, ya ce kwanaki biyu da suka gabata ne mataimakinsa ya dawo daga garuruwan Banki da Bama da Pulka, inda ya je domin kwashe kimanin 'yan gudun hijira 3,682 daga garin Banki zuwa Pulka.

Gwamnan ya bayyana cewa, 'yan tada kayar baya sun lalata gidaje 156,453 a jihar, yana mai cewa adadin shi ne kashi 30 cikin 100 na gidajen jihar.

Ya kuma bayyana jin dadinsa game da yadda sojoji suka karya lagon kungiyar, yana mai yabawa gwamnatin tarayya da rundunonin sojin kasar bisa nasarar da suka samu na durkusar da 'yan tada kayar bayan. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China