in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Nijeriya ta bukaci matasa su shiga a dama da su a fannin aikin gona
2017-05-13 11:32:49 cri
Gwamnatin Nijeriya ta yi kira ga matasa, su shiga a dama da su a harkokin aikin gona, domin inganta bangaren don tabbatar da wadatuwar abinci da rage matsalar tamowa a kasar.

Ministan aikin gona da raya karkara na kasar Audu Ogbeh ne ya yi kiran yayin wani taron kungiyar daliban fannin nazarin ayyukan gona ta kasar, da ya gudana a Abuja babban birnin kasar.

Audu Ogbeh ya ce shigar da karin matasa cikin harkokin gona, zai bunkasa kokarin kasar, na kara yawan albarkatun gona da take fitar da su tare da samun wadatuwar abinci.

Ministan ya ce gwamnati na kokarin amfani da ayyukan cibiyoyin bincike da jami'o'in nazarin aikin gona a yunkurinta na samar da fasahohin zamani da za su taimakawa matasa manoma inganta ayyukansu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China