in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manyan jami'an kasashen Sin da Cote d'Ivoire sun yi shawarwari a tsakaninsu
2017-05-22 20:57:26 cri
Shugaban majalisar tattalin arziki da zamantakewar al'ummar kasar Sin Du Qinglin ya yi shawarwari tare da takwaransa na kasar Cote d'Ivoire Diby.

Du Qinglin ya bayyana cewa, mu'amalar dake tsakanin majalisun tattalin arziki da zamantakewar al'umma na kasashen biyu wani muhimmin bangare ne na raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. Majalisar tattalin arziki da zamantakewar al'ummar kasar Sin za ta kiyaye yin mu'amala tare da bangaren Cote d'Ivoire bisa tunanin hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka mai dacewa da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, a kokarin samar da gudummawa wajen aiwatar da sakamakon da aka samu a gun taron koli na Johannesburg na dandalin hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka tare da raya dangantakar dake tsakanin Sin da Cote d'Ivoire.

A nasa bangare, Diby ya nuna yabo ga sakamako da aka samu a taron dandalin tattaunawar hadin gwiwar kasa da kasa bisa shawarar "ziri daya hanya daya", kana yana fatan majalisun biyu za su kara taka muhimmiyar rawa wajen inganta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China