in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojoji sun yi bore a kudu maso gabashin kasar Cote d'Ivoire
2017-02-08 21:10:25 cri
Rahotanni daga kasar Cote d'Ivoire suna cewa, wasu sojoji sun yi bore a wani sansanin sojojin musamman dake birnin Adiakéa, kudu maso gabashin kasar a jiya Talata, sai dai babu wanda ya mutu ko ya ji rauni.

Wasu sojojin musamman dake sansanin sun yi harbi cikin iska, daga baya suka mamaye manyan titunan wurin, inda suka kori jama'a zuwa gida. Haka kuma an rufe hukumomin gwamnati da makarantu da kantuna dake wurin. Bayanai na nuna cewa, wadannan sojoji son yi hakan ne don nuna rashin jin dadinsa ga matakin da gwamnati ta dauka a baya na baiwa wasu sojoji da suka tayar da bore kudi.

A jiya da yamma ne, hafsan hafsoshin sojojin kasar Cote d'Ivoire da babban hafsan sojojin musamman na kasar suka tashi zuwa Adiaké don yin shawarwari da wakilan sojojin da ke bore, amma ba a warware matsalolin da sojojin suke gabatar ba. Daga baya, wakilan sojojin sun bukaci yin shawarwari da ministan kula da harkokin tsaron kasa na fadar shugaban kasar Alain Richard Donwahi kai tsaye. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China