in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin tana son ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen ganin an shimfida zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya
2017-05-22 20:03:27 cri
Mamban majalisar harkokin kasar Sin Yang Jiechi ya gana da shugaban tawagar wakilan kungiyar kawancen kasashen Larabawa dake halartar taron koli na 14 na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Larabawa, inda Yang Jiechi ya bayyana cewa, Sin tana son ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen ganin an shimfida zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya.

Yang Jiechi ya bayyana cewa, kasar Sin ta yi nasarar gudanar da taron dandalin tattaunawar hadin gwiwar kasa da kasa game da shawarar "ziri daya hanya daya" da ya gudana kwanakin baya a nan birnin Beijing, kasashen Larabawa sun ba da muhimmiyar gudummawa, kuma kasar Sin tana son sa kaimi ga samun ci gaba tare da kasashen Larabawa bisa shawarar "ziri daya hanya daya". Sin tana goyon bayan kokarin kasashen Larabawa na tabbatar da 'yancin kabilu, kana tana son ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen ganin an samu zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin gabas ta tsakiya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China