in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fi mai da hankali kan batun ilimi da zaman lafiya a dandalin tattalin arzikin kasa da kasa
2017-05-21 13:31:28 cri
An kaddamar da taron manyan kusoshi na gabas ta tsakiya da arewacin Afirka na dandalin tattalin arzikin kasa da kasa, a Shuneh na kasar Jordan, a jiya Asabar, inda manyan 'yan siyasa da 'yan kasuwa fiye da 1100, wadanda suka zo daga kasashe fiye da 50, suka halarci taron. Kuma batutuwan da suka fi janyo hankalinsu a wajen taron su ne, ayyukan samar da guraben aiki ga matasa, da kokarin sanya su cikin makaranta, gami da kiyaye zaman lafiya a gabas ta tsakiya.

Yayin wannan taro, wasu shugabanni na kasashe daban daban sun yi jawabai, inda shugaban kasar Nijar Mahamadou Issoufou ya ce, matakin da za a iya dauka don daidaita matsalar kwararowar 'yan gudun hijira daga Afirka zuwa Turai shi ne, kyautata sha'anin ilimi, da kara samar da guraben ayyukan yi.

A nasa bangaren, yariman kasar Jordan, Hussein bin Abdullah, ya yi kira ga gamayyar kasa da kasa da su taimakawa matasan duniya, musamman ma na gabas ta tsakiya, a kokarinsu na kafa kamfanoni masu zaman kansu.

Yayin da babban sakataren zartaswa na dandalin tattalin arzikin kasa da kasa, Klaus Schwab, ya yi kira ga shugabannin kasashen dake gabas ta tsakiya, da su kara sauraron shawarwarin matasa, kafin su yanke shawara kan wasu harkokin siyasa.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China