in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin tana kokarin taka muhimmiyar rawa kan harkokin yankin gabas ta tsakiya
2017-03-22 20:31:20 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a nan birnin Beijing a yau Laraba cewa, Sin ba 'yar kallo ba ce a harkokin yankin gabas ta tsakiya.

A kwanakin baya, sarkin Saudiyya da firaministan Isra'ila sun ziyarci kasar Sin. Wasu kafofin watsa labaru na kasashen yammacin duniya dai na yayata cewa, Sin ba ta taka muhimmiyar rawa kan batutuwan da suka shafi yankin gabas ta tsakiya, yayin da a yanzu take kokarin shiga harkokin yankin.

Game da wannan batu, Hua Chunying ta bayyana cewa, Sin tana tsayawa tsayin daka kan manufar adalci, tana kuma taka muhimmiyar rawa, wajen warware batutuwan Palesdinu da Isra'ila, da harkar nukiliyar Iran, da batun Syria, da dai sauransu ta hanyar siyasa.

Uwar gida Hua ta ce Sin tana fatan ci gaba da kwazo tare da kasashen dake bin manufar "ziri daya da hanya daya", ciki har da kasashen yankin gabas ta tsakiya, wajen more fasahohi, da zurfafa hadin gwiwarsu, yayin da suke bude kofa da yin mu'amala da juna. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China