in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Sin za ta yi garambawul a fannin kamfanonin mai da iskar gas
2017-05-22 10:17:22 cri
Hukumomin kasar Sin sun sanar a jiya Lahadi cewa za'a yi garambawul a fannin kamfanonin mai da iskar gas na kasar, inda gwamnatin ta kudiri aniyar sakarwa 'yan kasuwa mara domin su samar da yanayi mai inganci a fannin ta yadda za'a samu gogayya a fannin hada hadar albarkatun mai da iskar gas.

Wannan shiri tuni ya samu amincewar kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin CPC, da kuma majalisar gudanar da sha'anin mulki ta kasar Sin.

A karkashin wannan sabon tsarin, 'yan kasuwa su ne ke da alhakin aiwatar da harkokin rarraba mai a kasar, kuma gwamnati za ta dauki alhakin sa ido ne wajen kula da tabbatar da tsaron makamashi na kasa, da kuma tabbatar da ganin albarkatun suna biyan muradun jama'ar kasa baki daya.

A yanzu dai an bayyana wannan shiri da aka jima ana sa ran gabatar da shi wanda a halin yanzu mahukuntan kasar Sin suka yi amanna cewa sabon tsarin zai tabbatar da ingantuwar al'amurra a kasar ta biyu mafi karfin tattalin arziki a duniya.

Garambawul din yana kunshe ne cikin shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 13 na shekarar 2016 zuwa ta 2020.

Shirin yana kara tabbatar da aniyar mahukuntan kasar wajen zurfafa yin gyare gyare a kamfanonin mai da iskar gas mallakar gwamnatin kasar, kuma zai baiwa kamfanoni damar samun karuwar masu zuba jari a fannin albarkatun mai da iskaar gas. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China