in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zambia ta lashi takobin ci gaba da gyara harkokin kasuwanci dan jan hankalin masu zuba hari
2017-05-18 11:04:34 cri
Gwamnatin kasar Zambia ta ce za ta ci gaba, da aiwatar da garambawul ga harkokin kasuwanci ta yadda za su jan hankalin masu zuba jari.

Mataimakiyar shugaban kasar Inonge Wina, ta ce Gwamnati da hadin gwiwar masu ruwa da tsaki, kamar bankin duniya da bangarori masu zaman kansu, za ta aiwatar da sauye-sauye a tsarin kasuwanci da nufin saukaka matakan yin kasuwanci a kasar.

Kafar yada labarai ta kasar ta ruwato cewa, a jawabin da ta gabatar yayin taron saukaka harkokin kasuwanci a kasar na 2017 da ya gudana a birnin Livingstone dake kudancin kasar, mataimakiyar shugaban kasar ta Zambia, ta ce gwamnati ta bijiro da jerin sauye-sauye dake da nufin magance kalubalen da bangarori masu zaman kansu ke fuskanta, tana mai cewa za kuma a ci gaba da gudanar da sauye-sauyen. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China