in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Zambia ya ki amincewa da kada kuri'ar raba gardama saboda matsalolin kudi
2017-03-09 11:46:48 cri
Shugabn kasar Zambia Edgar Lungu, ya ce ba zai amince da matsin lambar da ake masa na kada kuri'ar raba gardama kan kudurin dokar hakkokin al'umma ba saboda matsalar rashin kudi.

A makon da ya gabata ne hadakar kungiyoyin al'umma a kasar suka kaddamar da wani gangami domin matsawa gwamnati shirya kada kuri'a kuri'ar raba gardama kan kafa dokar kare hakkokin al'umma, bayan wanda aka yi tare da babban zaben kasar a shekarar da ta gabata ya lalace.

Kungiyoyin da daidaikun mutane na fafutukar tabbatar da bin ka'idojin doka da kuma sanya kudurin dokar fadada hakkokin al'umma cikin kundin tsarin mulkin kasar da aka yi wa gyaran fuska. ( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China