in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Zambia ta hana jami'an 'yan sanda auren 'yan kasashen waje
2017-01-24 09:44:25 cri
Rundunar 'yan sandan kasar Zambia ta umarci jami'an ta da su kauracewa auren baki 'yan kasashen waje, kana wadanda suka riga suka yi irin wannan aure, su gaggawa gabatarwa rundunar bayanin abokan zaman na su cikin mako guda, ko kuma su fuskanci matakin ladaftarwa.

Tuni dai shugabar rundunar Kakoma Kanganja, ta fidda takardar umarnin, tana mai cewa sashe na 3 da na 5 na doka ta 103, ta ayyukan 'yan sanda ta tanaji wannan mataki, sai dai kuma da yawa daga jami'an rundunar na yin watsi da dokar.

Uwar gida Kanganja, ta ce mai yiwuwa masu leken asiri na kasashen waje, su yiwa kasar kutse ta hanyar auren jami'an 'yan sanda, wanda hakan zai iya bada damar bankadar sirikan kasar cikin sauki.

Tuni dai wannan umarni ya fara shan suka daga wasu 'yan kasar, wadanda suke ganin aiwatar da shi ba shi da wata fa'ida.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China