in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin da hukumomin UNICEF da UNFPA za su fadada hadin gwiwa karkashin shawarar ziri daya da hanya daya
2017-05-18 09:29:22 cri
Mataimakiyar firaministan kasar Sin Liu Yandong, ta ce kasar Sin na duba yiyuwar karfafa hadin gwiwa da hukumomin MDD da suka hada da asusun kula da kananan yara UNICEF da asusun kula da yawan al'umma UNFPA, karkashin shawarar 'ziri daya da hanya daya'.

Liu Yandong ta bayyana haka ne a ranar Talata, yayin tattaunawar da ta yi a mabanbantan lokuta da Babban Darktan UNICEF Anthony Lake da takwaransa na hukumar UNFPA Babatunde Osotimehin, wadanda suka halarci taron shawarar 'ziri daya da hanya daya' dake da nufin karfafa hadin gwiwa da kasashen duniya, wanda ya gudana a ranakun 14 da 15 na watan Mayu, a nan birnin Beijing.

Shawarar ziri daya da hanya daya na da nufin samar da kyakkyawan yanayin samun ci gaban tattalin arzikin yankuna da duniya baki daya, da taimakawa kasashen da ke kan hanyar da shawarar ta shafa amfana daga dammamakin da ci gaban kasar Sin ta samar tare da samun ci gaba na bai daya.

Da suke jinjinawa irin nasarori da kasar Sin ta samu wajen kare hakkokin yara da ciyar da al'umma gaba, da kuma taya ta murnar nasarar da taron ziri daya da hanya daya ya samu, Anthony Lake da Bababtunde Osotimehin, sun ce a shirye suke su karfafa hadin gwiwa da kasar Sin karkashin shawarar, ta yadda za a samu damar cimma muradun ci gaba masu dorewa kawo shekarar 2030. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China