in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya gana da takwaransa na Kenya
2017-05-15 21:25:01 cri
A yau Litinin ne,shugaban kasar Sin ya gana da takwaransa na kasar Kenya Uhuru Kenyatta, wanda ya halarci taron dandalin hadin gwiwar kasa da kasa na kwanaki biyu game da shawarar ziri daya hanya daya da aka kammala a yau a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin

A yayin ganawar, shugaba Xi Jinping ya bayyana cewa, Kenya na daga cikin kasashen Afirka da ake gwajin hadin gwiwar masana'antu a tsakaninsu da Sin, wadda kuma ke zama abin koyi a hadin gwiwar dake tsakanin Sin da kasashen Afirka. Ya ce, kasarsa tana fatan hada kai da kasar Kenya domin daga matsayin dantankatar dake tsakanin kasashen biyu zuwa wani sabon matsayi.

Uhuru Kenyatta daga nasa bangaren ya ce, taron dandalin da aka gudanar a wannan karo ya nuna wa duniya baki daya nasarorin da aka samu a shawarar ziri daya hanya daya, wanda kuma ya samar da dandalin da kasashe masu tasowa da kuma masu sukuni za su rika tattauna yin hadin gwiwa bisa tushen samun moriyar juna. Kenya tana son shiga a dama da ita wajen raya "ziri daya hanya daya", tare da karfafa hadin gwiwa da kasar Sin a fannonin tattalin arziki da zuba jari da makamashi da yawon shakatawa da kuma muhimman ababen more rayuwa. (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China