in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'an tsaro a Najeriya sun damke dan kasuwa bisa zargin gurgunta tattalin arzikin kasar
2017-05-07 12:10:46 cri
Jami'an tsaro na DSS a Najeria sun sanar da cewa, a jiya Asabar ne suka cafke Ifeanyi Ubah, mai kamfanin mai na Capital Oil, bisa zarginsa da yin kafar ungulu wajen gurgunta tattalin arzikin kasar.

Mai magana da yawun hukumar tsaro ta DSS Tony Opuiyo , ya fada cikin wata sanarwar da ta iske kamfanin dillancin labarai na Xinhua a Legas birnin kasuwanci na kasar cewar, an kama hamshakin dan kasuwar tare da wasu 'yan siyasa a ranar Jumma'ar da ta gabata, saboda zarginsa da laifin sace man fetur wanda hukumar man fetur ta kasar (NNPC) ta ajiye a gidan mansa a birnin Ikko.

An kiyasta kudin man ya kai naira biliyan 11 kwatankwacin dala miliyan 34.

Opuiyo ya kara da cewa, matakin da Ubah ya dauka tamkar yin zagon kasa ne ga tattalin arzikin kasar, kuma matakin zai iya yin illa ga ci gaban tattalin arzikin Najeriyar, kana lamarin barazace ga zaman lafiyar kasar kuma ya saba dokar gwamnati. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China