Kakakin rundunar 'yan sandan Murtala Ibrahim ya bayyana cewa, an tunkari 'yan kunar bakin waken, wadanda suka yi jigida da ababen fashewa a kofar shiga bataliya ta 195 na rundunar sojin Nijeriya dake birnin Maiduguri.
Murtala Ibrahim ya ce, 'yan kunar bakin waken sun tada bam din dake jikinsu, al'amarin da ya yi sanadin mutuwarsu tare da raunata wani soja guda.
Ya kuma shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua tuni harkokin suka koma daidai a wajen da al'amarin ya auku, bayan jami'an sashen kwance bam na rundunar sun tabbatar da babu sauran barazana.
Hukumar bada agajin gaggawa ta kasar NEMA, ta ce 'yan kunar bakin waken 'yan mata ne matasa. (Fa'iza Mustapha)