in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD: Ayyukan Boko Haram na cin zarafin kananan yara a Nigeria
2017-05-05 10:04:15 cri
Rahoton farko na sakatare Janar na MDD Antonio Guterres kan yara da ayyukan ta'addanci Nijeriya, ya ce ayyukan kungiyar Boko Haram a yankin arewa maso gabashin kasar na ci gaba da jefa yara maza da mata cikin mawuyacin hali.

Yayin taron manema labarai na kulla-yaumin, kakakin MDD Stephane Dujarric, ya ce sabon rahoton ya bayyana irin tasirin da tabarbarewar tsaro da ayyukan jin kai ya yi a kan yara a kasar, tsakanin watan Junairun 2013 zuwa Decemban 2016.

Wakiliyar Sakatare Janar din na musammam kan harkokin yara da rikice-rikice Virginia Gamba, ta ce ayyukan Boko Haram sun jefa matsanancin tsoro a zukatan yaran dake yankin arewa maso gabashin Nijeriya da kasashe makwabta.

Tsakanin lokacin hada rahoton, hare-haren Boko Haram kan al'ummomi da arangama tsakaninta da Jami'an tsaro, sun yi sanadin mutuwar yara 3,900 tare da jikkata wasu 7,300.

Nijeriya dai, ta samu gagarumin nasara a yaki da take da Boko Haram, inda jami'an tsrao dake yankin da al'amarin ya fi kamari su ka fatattaki mayakan daga maboyarsu dake dajin Sambisa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China