in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Boko Haram ta sako 'yan matan Chibok 82
2017-05-07 11:43:58 cri
Wata majiya daga gwamnatin Najeriya ta shedawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa kimanin 'yan matan sakandaren Chibok 82 daga cikin 200 da mayaka Boko Haram suka sace a shekarar 2014 ne aka sako su a jiya Asabar daga hannun mayakan dake tsare da su a jahar Borno dake arewa maso gabashin kasar.

Majiyar ta shedawa Xinhua cewa, an sako 'yan matan ne biyowa bayan wata yarjejeniyar da aka cimma tsakanin gwamnatin Najeriyar da mayakan masu tsattsauran ra'ayi.

Sakin 'yan matan ya zo ne wata guda bayan da shugaban Najeriyar Muhammadu Buhari ya bayyana cewa gwamnatinsa tana kokarin yin hadin gwiwa da hukumomin kasashen waje masu shiga tsakani domin ganin an sako 'yan matan na sakandaren Chibok.

Shugaban na Najeriya ya fada a ranar 14 ga watan Aprilun a cikin wata sanarwar da ya gabatar yayin da 'yan matan ke cika shekaru 3 da yin garkuwa da su inda ya bayyana cewa, a shirye gwamnatinsa take ta tabbatar an sako 'yan matan na Chibok.

Shugaba Buhari ya ce, gwamnati na ci gaba da tuntubar masu shiga tsakani da kuma hukumomin tsaro na sirri na cikin gida domin tabbatar da sakin raguwar 'yan matan da sauran mutanen da mayakan na Boko Haram ke yin garkuwa da su.

Kana ya shedawa iyayen yaran da sauran 'yan Najeriya cewa, kada su fidda tsammanin dawowar raguwar 'yan matan na sakandaren Chibok da ake garkuwa da su. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China