in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankin Duniya ya tallafawa shirin sauyin yanayi na kasar Ghana da dala miliyan 5.5
2017-04-28 10:20:28 cri
Bankin duniya ya ce zai tallafawa al'ummun kasar Ghana 52, wajen aiwatar da shirin kula da albarkatu bisa wata hanya mai dorewa.

Wata sanarwar da ofishin bankin dake Ghana ya fitar jiya Alhamis, ta ce wasu al'ummu da aka zaba a yankunan karkara na Brong-Ahafo da yankin yammacin kasar ne za su ci gajiyar tallafin na dala miliyan 5.5.

An tsara shirin ne, ta yadda zai karfafa ilimi da harkokin al'ummun wajen rage lalacewar dazuka da inganta kula da harkokinsu.

Haka zalika, shirin na da nufin kara musu kwarin gwiwa wajen tunkarar matsalolin da dan Adam da kuma sauyin yanayi ke haifarwa

Daraktan Bankin a kasar Ghana Henry Kerali, ya ce shirin zai bada gudunmuwa ga shirin kawance na bankin a kasar Ghana, tare da magance batutuwan sauyin yanayi ta hanyar tallafawa shirye-shirye masu jibi da samar da ruwa da da kare lallacewar filaye. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China