in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Ghana ta yi kiran da a samar da tsarin adana bayanai don kare kasuwanci ta yanar gizo
2017-04-21 09:34:33 cri
Ministar sadarwa ta kasar Ghana Ursula Owusu-Ekuful ta jaddada bukatar kara adana muhimman bayanai a kan iyakokin kasar, don kare bayanai da suka shafi kasuwannin ta yanar gizo.

Ministar ta bayyana hakan ne yayin da ta ke jawabi a taron karawa juna sani game da adana bayanai na kasa da kasa karo biyu wanda hukumar kare bayanai ta shirya. Ta kuma lura da cewa, muhimman bayanai tamkar makamashi ne da ke bunkasa harkokin kasuwanci ta yanar gizo a wannan zamani, don haka ta nuna damuwa kan yadda ake da bukatar kara tsaron bayanai.

Ministar ta kuma yi kiran da a kara daukar matakan kare bayanai, ganin yadda harkokin kasuwanci na kasa da kasa suka dunkule a waje guda. A cewarta yana da muhimmanci a kara fahimtar yadda kasashe da shiyoyi da kasa da kasa ke kokarin bullo da matakai da dokoki wadanda za su saukaka harkokin kasuwanci da cinikayya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China