in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Kenya ya ce hadin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro na taimakawa wajen yaki da ta'addanci
2017-05-04 09:07:44 cri
Shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta, ya ce aiki kafada-da-kafada tsakanin hukumomin tsaro ya taimakawa gwamnati wajen kawo karshen nau'in laifuffuka da dama, ciki har da ta'addanci.

Uhuru Kenyatta ya yi kira ga hukumomin tsaro su samar da wasu dabaru da za a rika amfani da su tsakanin hukumomin daban-daban, wanda ya ce ya taimakawa kasar ganowa tare da datse hanyoyin sadarwa tsakanin 'yan ta'adda.

Ya ce tilas ne hukumomin tsaro su dai na amfani da tsarin nan na kin musayar bayanai, tun da ya gaza haifar da mai ido.

Shugaban kasar ya yi bayanin cewa, hadin gwiwa tsakanin hukumomin sabanin tsarin na kin musayar bayanai, ya cimma nasarori wajen ganowa da karewa da kuma datse manufofi da ayyukan kungiyoyin 'yan ta'adda.

Shugaban na wannan bayani ne yayin yaye kashi na 19 na manyan jami'an soji. Wannan shi ne karon farko da shugaban kasar ya yi jawabi ga jami'an tsaro dake karbar horo a kwalejin horas da sojoji. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China