in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin: Kamata ya yi a aiwatar da kudurin kwamitin sulhun MDD game da batun Koriya ta Arewa
2017-04-27 10:40:55 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya ce kamata ya yi bangarori daban daban su aiwatar da kudurin kwamitin sulhun MDD game da batun Koriya ta Arewa a dukkan fannoni. Mr. Wang ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da 'yan jarida, tare da mataimakin shugaban gwamnatin kasar Jamus, kuma ministan harkokin wajen kasar Sigmar Gabriel a birnin Berlin a jiya Laraba.

Mr. Wang Yi ya jaddada cewa, dukkan kudurorin da kwamitin sulhun MDD ya gabatar na kunshe ne cikin fannoni biyu. Na farko shi ne nuna adawa da manufar kasar Koriya ta Arewa ta mallakar makaman nukiliya, da daukar matakan hana kasar kera makamai masu linzami na nukiliya. Na biyu shi ne jaddada warware batun cikin lumana, da magance daukar matakan da ka iya tsananta halin da ake ciki, da ci gaban shawarwari a tsakanin bangarori shida cikin hanzari.

Ya ce kamata ya yi a aiwatar da kudurin kwamitin sulhun a dukkan fannoni, ba wai kawai biyan bukatun wasu bangarorin su kadai ba. A cewarsa gwajin makamai masu linzami na nukiliya ya sabawa kudurin kwamitin sulhun, amma yin atisayen soja a zirin Koriya, shi ma bai dace da manufar kudurin ba.

Wang Yi ya ce, Sin ta tsaya tsayin daka kan manufar kawar da makaman nukiliya a zirin Koriya, da kafa tsarin zaman lafiya a zirin. A hannu guda Sin na fatan ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen cimma wadannan burika. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China