in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Iran sun rattaba hannu kan yarjejeniyar sake fasalin cibiyar nukiliya ta Arak
2017-04-24 11:20:22 cri
Kasashen Sin da Iran sun rattaba hannu kan wata kwangila, ta wadda ya jibanci sakewa cibiyar sarrafa makamashin nukiliyar Iran dake Arak fasali, yayin wani zama da wakilan sassan biyu suka yi a birnin Vienna a jiya Lahadi.

Wannan mataki dai wani bangare ne na yarjejeniyar da kasashen 5 tare da Iran din suka amincewa, karkashin shirin JCPOA, yayin shawarwari game da shirin Iran din na sarrafa makamashin nukiliya da ya gudana a birnin Vienna cikin watan Yulin shekarar 2015.

Karkashin yarjejeniyar ta Vienna, Iran ta amince da ta sake fasalin wannan cibiyarta, ta yadda za ta rage yawan sinadarin plutonium da za a iya samarwa a cibiyar, tare da kaucewa sarrafa makamai masu alaka da sinadarin.

A kuma taron na Vienna ne kasashe 5 da suka kunshi Sin, da Amurka, da Rasha, da Faransa, da Jamus, da Birtaniya, tare da ita kanta Iran suka amince Sin da Amurka, su yi aiki tare wajen ganin an sauya fasalin waccan cibiya ta Arak. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China