in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Iran da Rasha za su hada hannu wajen ginin tashoshin makamashin Nukiliya
2017-04-19 10:56:15 cri
Ministan Makamashi na Iran Hamid Chitchian, ya ce Iran za ta fara ginin tashoshin makamashin nukiliya biyu a kasar, da hadin gwiwar kwararru daga kasar Rasha.

An rattaba hannu kan kwangilar ne tsakanin hukumar kula da kafawa da da ayyukan makamashi ta Iran AEOI da kuma Rasha, inda ake dab da fara ginin tashoshin nukiliya guda biyu masu karfin megawatt 1,000.

Wannan jawabin na zuwa ne, bayan shugaban hukumar AEOI Ali Akbar Saleh ya sanar a ranar Asabar cewa, nan bada jimawa ba za a fara ginin tashoshin biyu.

Hamid Chitchian ya kara da cewa, akwai wani aikin dake bisa hanya tsakanin ma'aikatar makamashin da Moscow, inda za a gina tashar makamashi mai karfin nmegawatt 1, 400 a lardin Hormozgan dake kusa da mashigin ruwan Persha, ya na mai cewa tuni aka fara aikin ginin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China