in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Saurin bunkasuwar tattalin arzikin yankin Afirka dake kudu da hamadar Sahara ya karu
2017-04-24 09:56:23 cri
Bisa labarin da jaridar The Guardian ta kasar Tanzania ta bayar a kwanakin baya, an ce, bisa rahoton da bankin duniya ya gabatar, ko da yake tattalin arzikin kasashen yankin kudu da hamadar Sahara na Afirka ya ragu sosai a shekarar 2016, da adadin da ya dara na shekaru fiye da 20 da suka gabata, amma tattalin arzikin yankin a shekarar nan ta 2017 yana karuwa. Ana kuma sa ran cewa, yawansa zai karu da kashi 2.6 cikin dari bisa na bara.

Bisa rahoton da aka gabatar, an ce, kasashe 7 wato Tanzania, Cote d'Ivoire, Habasha, Kenya, Mali, Ruwanda da Senegal dake yankin kudu da hamadar Sahara na Afirka, suna ta bunkasa tattalin arzikinsu. Kaza lika yawan mutanen dake kasashen 7 ya kai kashi 27 cikin dari bisa jimillar al'ummun yankin baki daya. Yayin da yawan GDPn nasu ya kai kashi 13 cikin dari, kana saurin bunkasuwar tattalin arzikinsu a kowace shekara tun daga shekarar 2015 zuwa 2017, ke karuwa da kashi fiye da 5.4 cikin dari.

Babban masanin tattalin arziki mai kula da yankin Afirka na bankin duniya Albert Zeufack ya bayyana cewa, kyautata yanayin zuba jari, da sa kaimi ga yin kwaskwarima don karfafa samar da kaya a masana'antun kasashen Afirka, da ma samar da yanayin tattalin arziki mai kyau, su ne dalilai na tabbatar da kiyaye bunkasuwar tattalin arzikin yankin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China