in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
IMF ya ce Bunkasar tattalin arzikin kasar Sin ya zarce hasashen da aka yi
2017-04-22 13:53:47 cri
Mataimakin shugaban sashen dake kula da harkokin kasashen Asia-Pacific na Asusun ba da lamuni na duniya IMF, Markus Rodlauer ya ce, cikin watanni uku na farkon shekarar bana, tattalin arzikin kasar Sin ya bunkasa cikin sauri da yanayi mai kyau, inda ya ce mai iyu wa ne, Asusun IMF ya kara adadin hasashen da ya yi kan ci gaban tattalin arzikin kasar a bana.

Mr. Rodlauer ya bayyana haka ne a jiya Juma'a, yayin taron manema labarai da aka yi mai taken "hasashen habakar tattalin arziki a yankin Asia-Pacific".

Ya kara da cewa, ci gaban tattalin arzikin kasar Sin a cikin watanni uku na farkon shekarar nan ya wuce hasashen da Asusun ya fidda a baya, musamman ma la'akari da karuwar alkaluman GDP a cikin wadanan watanni, inda ya kai kashi 6.9 cikin dari, idan aka kwatanta da na makamancin lokacin a bara.

Shi ya sa, cikin sabon rahoton da Asusun ya fidda game da hasashen da aka yi kan tattalin arzikin kasashen duniya, aka canza adadin bunkasar tattalin arzikin kasar Sin da aka yi a watan Juanirun bana daga kashi 6.5 zuwa kashi 6.6 cikin dari.

Har ila yau, ya ce gwamnatin kasar Sin ta riga ta dauki wasu matakai na hana karuwar farashin gidaje cikin sauri a wasu wurare na kasar, da kuma rigakafin matsalolin da za a iya fuskanta a fannin sha'anin kudi. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China