in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata kasashen Afirka su hada kai da kasar Sin wajen aiwatar da shirin aiki na Johannesburg
2017-04-21 20:39:24 cri

Yau Jumma'a ne ministan harkokin wajen kasar Eritrea Osman Saleh, ya ce yana fatan kasashen Afirka za su jure wahalar da suke fuskanta, su kuma warware matsalolinsu a gida. Kaza lika su hada kai da kasar Sin wajen aiwatar da shirin aiki da aka amincewa na taron Johannesburg, karkashin dandalin tattaunawar hadin gwiwa a tsakanin kasashen Sin da Afirka, a kokarin kara kawo wa jama'ar Afirka alherai.

Osman Saleh ya fadi hakan ne yayin da yake zantawa da wakilin kamfanin dillancin labaru na Xinhua a wannan rana.

Osman Saleh dai ya shafe kwanaki 6 yana ziyarar aiki a nan kasar Sin, bisa gayyatar da takwaransa na kasar Sin Wang Yi ya yi masa. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China