in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zuba jari da kasar Sin ke yi a fannin samar da kayayyakin more rayuwa jigo ne wajen cigaba Afrika
2017-04-03 13:19:48 cri
Wani jami'in MDD ya bayyana cewa, zuba jari da kasar Sin take yi a fannin samar da kayayyakin more rayuwa ya kasance babban jigo na burin cigaban da nahiyar Afrika ke da shi.

Nicholas Rosellini, jami'in MDD game da kasar Sin, ya shedawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewar jarin da kasar Sin ke zubawa a fannin makamashi, musamman ta hanyar samar da makamashi marar gurbata muhalli zai taimakawa nahiyar wajen samar da guraben ayyukan yi masu yawan gaske.

A bisa kididdiga, mutane miliyan 600 ne basu da hasken lantarki a Afrika.

Nicholas ya yabawa kasar Sin sabo da tallafawa kasashen Afrika da dama wajen samar da makamashi marar gurbata muhalli, ya ce baya ga rawar da Sin ke takawa wajen bunkasa cigaban tattalin arzikin nahiyar ta Afrika, hasken lantarki wani muhimmin jigo ne da ya shafi bukatu na rayuwar bil adama.

Jami'in ya bada tabbacin marawa kasar Sin baya karkashin shirin raya cigaban kasashen duniya na MDD wato UNDP domin ta samu zarafin aiwatar da shirye shirye da suka shafi cigaban nahiyar ta Afrika, musamman shirye shiryen da za su samarwa Afrikan cigaba mai dorewa.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China