in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Aikin asusun taimakawa Afirka a fannin ba da ilmi na Sin ya samu sakamako
2017-03-30 11:17:30 cri
A ranar 29 ga wata a cibiyar kungiyar UNESCO dake birnin Paris na kasar Faransa, an kaddamar da taron jinjinawa sakamakon da aka samu bisa mataki na farko da taron fara aiki na mataki na biyu na aikin samar da fasahohi ga horar da malamai a nahiyar Afirka da kungiyar UNESCO da asusun kasar Sin CFIT suka gudanar.

A gun taron, an ce, bayan da aka samu nasarar aikin bisa mataki na farko, gwamnatin kasar Sin ta kara samar da kudi dala miliyan 4 don tsawaita wa'adin gudanar da aikin da shekaru biyu. Kuma za a shigar da kasashen Togo da Zambia a cikin jerin kasashen da za a gudanar da aikin bisa mataki na biyu, don haka yawan kasashen da za su samu moriya daga aikin ya karu zuwa 10 a Afirka.

Babban direkta a fannin ba da ilmi na kungiyar UNESCO Tang Qian, ya yi jawabin bude taron, inda ya bayyana cewa, an samu nasarori wajen gudanar da aikin bisa mataki na farko. Aikin ya sa kaimi ga cimma burin samun bunkasuwa mai dorewa na MDD, musamman a fannonin ba da ilmi mai inganci da samar da damar yin karatu ga dukkan jama'a.

Zaunannen wakilin Sin dake kungiyar UNESCO Shen Yang, ya yi nuni da cewa, Sin za ta ci gaba da zurfafa hadin gwiwarta tare da kungiyar UNESCO don sa kaimi ga cimma ajandar samun bunkasuwa mai dorewa nan da shekarar 2030, musamman wajen samun zaman lafiya da 'yancin kai da bunkasuwa mai dorewa a nahiyar Afirka. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China