in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar Red Cross na neman tallafin kasar Sin game da bukatun jin kai a nahiyar Afrika
2017-03-27 10:20:02 cri
Kungiyar bada agaji ta duniya Red Cross na shirin hada hannu da kasar Sin domin inganta gudunmowar kayayyakin jin kai da kasar ke bayarwa tare da wayarwa da Sinawa kai domin su fahimci kalubalen jin kai da al'ummomin Afrika ke fuskanta.

Shugabar Kungiyar Red Cross a nahiyar Afrika Patricia Danzi wadda ta bayyana hakan, ta ce manufar ziyarar da ta yi niyyar kai wa Beijing cikin wannan wata ita ce, neman kara karfafa hadin gwiwa domin magance matsalar agajin jin kai da ake fuskanta a Afrika.

Da take ganawa da manema labarai a birnin Juba na kasar Sudan ta Kudu Patricia Danzi ta ce janyo hankalin Sinawa game da halin da ake ciki na da matukar muhimmanci saboda abu mafi wahala shi ne kawar da matsalolin.

Ta kara da yin kira ga masu bada gudunmowa, su gaggauta bayar da tallafi domin kare kara ta'zzarar al'amura a kasar Sudan ta Kudu da MDD ta ayyana matsalar yunwa a wasu sassan kasar, inda mutane 100,000 ke fuskanatar yunwa yayin da wasu miliyan daya ke gab da fuskantar yunwar.

Har ila yau, ta ce fada, da gudun hijira da rashin abinci mai gina jiki sun jefa lafiyar mutane cikin mawuyacin hali, ta na mai cewa, fari da rikice-rikice ya kara jefa al'ummomin kasashen Sudan ta Kudu da Somaliya cikin matsanancin hali. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China