in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masana na kasashen Iran, Rasha da Turkiya sun tattauna kan batun Syria
2017-04-21 12:34:24 cri
Rahotanni daga Kafofin watsa labarai na kasar Iran na cewa, Masana na kasashen Iran da Rasha da Turkiya sun tattauna kan batun Syria bisa tsarin shawarwarin shimfida zaman lafiya na Astana a birnin Tehran tun daga ranar 18 zuwa 19 ga wannan wata.

Kamfanin dillancin labaru na Mehr na kasar Iran ya ruwaito cewa, bangarorin uku sun tattauna kan batutuwan da suka hada da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a kasar Syria da musayar mutanen da aka yi garkuwa da su.

Ita ma tawagar masana ta MDD, ta halarci tattaunawar a matsayin mai sa ido.

A ranar 15 ga wannan wata ne, ministan harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov, da takwaransa na Iran Mohammad Javad Zarif, da kuma na Syria Walid Muallem, suka gana a birnin Moscow na Rasha, inda suka tattauna kan harin da Amurka ta kai wa Syria, da yin bincike kan harin makamai masu guba da hanyoyin samar da zaman lafiya a Syria, da hada hannu wajen yaki da ta'addanci.

Bisa yadda aka tsara, za a gudanar da sabon zagayen taron shimfida zaman lafiya na Astana, a farkon watan Mayu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China