in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi harbi a titin Champs Elysee dake birnin Paris na Faransa
2017-04-21 10:25:03 cri

Ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar Faransa ta bayyana a jiya cewa, wani mutum ya harbi wata motar 'yan sanda dake tsaya a titin Champs Elysee, harin da ya haddasa mutuwar wani dan sanda, tare da raunata wasu 'yan sanda biyu. Sai dai daga bisani an harbe maharin har lahira a wurin.

Kakakin ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar Faransa Pierre-Henry Brandet ya bayyanawa 'yan jarida a wannan rana cewa, an kaiwa 'yan sandan hari ne da gangan. Yanzu haka Ana kokarin tabbatar da asalin wanda ya kai harin, watakila akwai masu taimaka masa, 'yan sanda dai suna kokarin yin bincike game da musababin harin.

Kungiyar IS ta sanar da daukar alhakin kai harin ta hanyar kamfanin dillancin labaru na Amaq, tana mai cewa maharin dan kasar Belgium mamban kungiyar ne.

A jawabin da ya gabatar shugaban kasar Faransa François Hollande ya bayyana cewa, tuni mai gabatar da kara na kasar ya fara yin bincike kan batun. Ya ce, hukumomin kasar za su kara mai da hankali kan abubuwan da ke gudana a yayin babban zaben da za a yi a kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China