in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ghana ta ce a shirye ta ke ta taimakawa kasashen yankinta wanzar da tsaro a gabobin ruwa
2017-03-29 15:12:41 cri
Mataimakin shugaban kasar Ghana Mahamudu Bamumia ya bukaci kasashen Afrika su lalubo sabbin dabarun tsaron iyakokin ruwa.

Mahamudu Bamuwai ya ce Ghana ta kasance kasa mai cike da tsaro a yankin mashigin ruwan Guinea da ya fi ko ina fuskantar matsolilin bata gari a tekuna a fadin duniya.

Ya kara da cewa, kasarsa ta kuduri niyyar taimakawa makwaftan kasashe samun zaman lafiya da kwanciyar hankali, la'akari da cewa, duk abun da ya faru a yankin, zai iya tasiri ga sauran kasashe makwafta.

Mataimakin shugaban kasar na Ghana na wannan bayani ne yayin wani taron nahiyar Afrika karo na 3, matakan sanya ido a gabobin ruwa da baje kolin ayyukan Soji da ya gudana a Accra babban birnin kasar.

Taron ya samu halartar kwararru da masana kan tsaron gabar ruwa daga fadin duniya, inda suka tattauna kan hanyoyin magance barazana da tsaron gabobin ruwa ke fuskanta. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China