A Talatar nan ne firaministar kasar Birtaniya Theresa Marry May, ta sanar da cewa, za a gudanar da babban zaben kasar ta a ranar 8 ga watan Yunin bana, da zummar taimakawa gwamnatin kasar gudanar da shawarwari da kungiyar Tarayyar Turai, kan batun ficewar kasar daga kungiyar.
Haka kuma a yau din, madam May ta gabatar da jawabi a gaban fadarta, inda ta ce, an tsai da kudurin ne domin kara kiyaye moriyar kasar ta Birtaniya. (Tasallah Yuan)