in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bukaci a binciki kisan wasu jami'an agaji 3 a Sudan ta kudu
2017-04-16 12:54:37 cri
Babban jami'in bada agaji na MDD a Sudan ta kudu ya yi Allah wadai da kashe wasu jami'an hukumar da aka yi a garin Wau gari na biyu mafi girma a kasar, kana ya bukaci a gaggauta yin bincike.

Babban jami'in shirin jin kai na MDD dake kasar ta Sudan ta kudu, Eugene Owusu, ya ce kashe jami'an bada agaji ya faru ne a lokacin rabon muhimman kayayyakin abinci a garin Wau kasa da mako guda bayan kiran da aka yi na kawo karshen kaddamar da hare hare kan jami'an agajin a Sudan ta kudu.

A wata sanarwar da ya fitar a Juba, Owusu ya ce ya yi matukar kaduwa game da wannan mummunan al'amari, don haka ya bukaci a gaggauta binciko wadanda suka aikata wannan danyen aiki domin hukunta su.

An hallaka jami'an uku ne a lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa dakin ajiya na shirin hukumar samar da abinci ta duniya WFP, a lokacin da ake tsaka da fuskantar matsalar tsaro a garin Wau a ranar 10 ga wannan watan

Da wannan mutuwa, kawo yanzu ma'aikatan jin kai da aka hallaka a Sudan ta kudu sun kai 82, kuma a shekarar nan ta 2017 kawai, an hallaka jami'an agaji 14. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China