in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya: an dakile yunkurin kungiyar Boko Haram na kai hari ofisoshin jakadanci dake kasar
2017-04-13 09:31:32 cri
Hukumar tsaro ta farin kaya DSS a Nijeriya, ta ce ta dakile wani yunkurin kai hari kan ofisoshin jakadancin kasashen Amurka da Birtaniya, dake Abuja, babban birnin kasar cikin watan da ya gabata.

Wata sanarwa da kakakin hukumar ta DSS Tony Opuiyo ya fitar a jiya, ta ce bayan gudanar da bincike, hukumar ta kama mayakan Boko Haram guda biyar dake da alaka da kitsa harin.

Tony Opuiyo ya ce an kama mutanen ne a jihar Benue dake arewa maso tsakiyar kasar cikin watan Maris din da ya gabata.

Gwamnatin Nijeriya dai ta samu gagarumar nasara a yaki da take da kungiyar Boko Haram, inda cikin watan Disamban da ya gabata, jami'an tsaro dake aiki a yankin da ayyukan kungiyar ya fi kamari, suka fattakin 'ya'yan kungiyar daga dajin Sambisa da ya kasance tungarsu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China