in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya za ta seta tunanin wadanda rikicin Boko Haram ya shafa
2017-04-12 09:40:49 cri
Wani jami'i a Najeriya ya ce gwamnatin kasar za ta samar da wata cibiyar gyaran tunani ga mutanen da rikicin Boko Haram ya shafa a shiyyar arewa maso gabashin kasar.

Osagie Ehanire, shi ne karamin ministan lafiya na Najeriya ya fada a taron manema labarai a Maiduguri cewa, kafa cibiyar na daga cikin matakan da gwamnatin kasar ke dauka na farfado da tunanin mazauna yankunan masu fama da rikice rikice.

Ehanire ya ce kafa cibiyar kula da tunanin mutanen da rikicn Boko Haram din ya shafa na daya daga cikin kudurorin gwamnatin shugaban Muhammadu Buhari na sake gina wannan yankin.

Ministan ya kara da cewa, za'a tura jami'an kula da lafiya cibiyoyin kiwon lafiyar da aka tanada, ya ce wasu daga cikin jami'an za su bi gida gida domin ba da kulawa ga al'ummomin wadancan yankunan.

Boko Haram ta hallaka mutane sama da 20,000, kana wasu miliay 2.3 sun tsere daga gidajensu daga shekarar 2009. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China