in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wata kotu a Najeriya ta hukunta wadanda suka yi garkuwa da tsohon dan takarar shugaban kasa
2017-04-11 10:52:19 cri
A jiya Litinin wato kotu a Najeriya ta zartar da hukuncin daurin rai da rai kan wasu Fulani su 7 wadanda aka samu da laifin yin garkuwa da tsohon dan takarar shugabancin kasar Olu Falae.

Kotun wanda take zamanta a Akure, babban birnin jahar Ondo, ta samu mutanen 7 ne da aikata laifin yin garkuwa da tsohon dan takarar wanda gwamnatin jahar ta shigar da karar.

Haka zalika, ana zargin mutanen da laifin shirya fashi da makami, wadannan su ne biyu da cikin laifukan da ake tuhumar mutanen da aikatawa.

Falae wanda ya kasance tsohon sakataren gwamnatin tarayya, kuma tsohon ministan kudin kasar, an yi garkuwa da shi ne a gidan gonarsa dake kauyen Ilado a kudu maso yammacin birnin Akure na jahar ta Ondo a ranar 21 ga watan Satumbar bara, kafin daga bisani aka sako shi 'yan kwanaki bayan yin garkuwa da shi. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China