in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu mata biyu 'yan kunar bakin wake sun hallaka kansu a Najeriya yayin harin da bai yi nasara ba
2017-04-11 09:30:28 cri
A Najeriya wasu mata biyu 'yan kunar bakin wake sun gamu da ajalinsu bayan da wasu boma bomai dake daure a jikinsu suka tashi da su a jiya Litinin a Maiduguri babban birnin jahar Borno dake arewa maso gabashin kasar, yayin da jami'an tsaron kasar suka dakile wannan harin inda suka hana su shiga inda suka shirya kaddamar da harin.

Mai magana da yawun hukumar bada agajin gaggawa ta kasar NEMA, ya shedawa kamfanin dillacin labarai na Xinhua cewa, jami'an tsaron sun tsare mata 'yan kunar bakin waken ne, inda suka dakile harin da suka kuduri aniyar kaddamarwa a kusa da jami'ar Maiduguri.

Kakakin na NEMA ya ce ba'a samu hasarar rayuka ko jikkata ba, bayan matan biyu 'yan kunar bakin waken da suka mutu nan take.

Wannan yunkurin kai harin ya zo ne kwanaki biyu bayan wani harin da aka kai wani masallaci a birnin na Maiduguri. Harin ya raunata mutane hudu a karshen mako, kamar yadda hukumomin yankin suka tabbatar.

Birnin na Maiduguri inda a can aka kyankyashe kungiyar ta Boko Haram, kuma birnin ya kasance a matsayin hedkwatar mayakan Boko Haram a shekaru da dama, kafin daga bisani dakarun Najeriya suka fatattaki mayakan daga babbar maboyarsu a watan Disambar bara.

Hare haren mayakan na Boko Haram, ya yi sanadiyyar hallaka mutane sama da 20,000 kuma ya raba mutane sama da miliayn 2 da dubu 300 da gidajensu daga shekarar 2009 zuwa yanzu. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China