in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Nijeriya ta lashi takobin ci gaba da yaki da cin hanci
2017-04-12 09:53:08 cri
Gwamnatin Nijeriya ta ce shari'o'in yaki cin hancin da aka kammala a baya-bayan nan ba za su sanyaya gwiwar ta a yaki da take da cin hanci ba, tana mai alkawarin cewa, sakamakon shari'o'i da aka yanke a matakin babbar kotun kasar, da suka yanke wadanda ake tuhuma da cin hanci, ba za su hana ta yaki da mummunar dabi'ar ba.

Cikin wata sanarwa da ya fitar jiya Talata, Ministan yada labarai da al'adu na kasar Lai Muhammad, ya tabbatar da cewa, gwamnatin ta daukaka dukkan shari'o'in a matakin kotun daukaka kara, inda za ta yi binciken kwa-kwaf kan shari'o'in.

Lai Muhammad ya ce ana sake nazari na tsanaki kan hukunce-hukuncen, domin tantance ko matsalar tana daga bangaren gwamnati, ko kuma kokarin mai da ta abun wasa ake yi.

Ya ce yaki da cin hanci da rashawa abu ne mai wahala kuma zai shafe lokaci mai tsaho, amma gwamnati ta shirya tsaf don tunkarar aikin.

Har ila yau ya kara da cewa, dole ne gwamnati ta yi nasara domin ka'idojin doka da jama'a na mara mata baya, yana mai cewa, somin tabi kawai aka yi, don haka, babu wani abu da zai dauke hankalinta koma ya sanyaya mata gwiwa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China