in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rasha ta ce bangaren adawa na Syria na neman uzuri na rashin halartar taron neman sulhu
2017-03-15 09:39:48 cri
'Yan tawayen Syria sun ce farmaki ta sama da dakarun Rasha suka kai musu ne dalilinsu na kauracewa taron neman sulhu na Astana, yayin da Rashan ta ce uzuri kawai suke nema.

Jagoran wakilan Rasha, kuma wakilin musammam na Shugaban kasar ka rikicin Syria Alexander Lavrentiev, ya ce ba su ji dadin rashin halartar bangaren adawar Syria ba. Sai dai ya ce a ganinsu, kawai kirkirar uzuri suka yi.

An fara zagaye na uku na taron neman sulhu kan rikicin Syria a Astana babban birnin Kazakhstan ne a jiya Talata, inda ake gudanar da taron ta hanyar tuntubar bangarori biyu na kasar da sauran masu ruwa da tsaki.

Ana sa ran a gudanar da wani zaman taron a yau Laraba 15 ga watan Maris. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China