in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya: jihar Akwa Ibom ta yi shirin ko-ta-kwana don tunkarar cutar sankarau
2017-04-07 09:52:54 cri
Jihar Akwa Ibom mai arzikin man fetur dake kudancin Nijeriya, ta ce ta yi shirin ko-ta-kwana don tunkarar cutar sankarau da ta barke a wasu jihohi, da ma Abuja, babban birnin kasar.

Shugaban likitoci masu binciken musababbin barkewar cututtuka a cikin al'umma na jihar Akwa Ibom, Aniekeme Uwah, ya shaidawa manema labarai a jiya cewa, gwamnatin jihar ta umarci ma'aikatan kiwon lafiyar al'ummma, su zauna cikin shirin ko-ta-kwana don dakile yaduwar barkewar cutar.

Aniekeme Uwah ya ce duk da ba a samu bullar cutar a jihar ba, an dauki matakan yaki da ita, ciki har da samar da kibabbiyar cibiya ta bada daukin gaggawa.

An yi hasashen samun barkewar cutar dake bulla a lokacin zafi a Nijeriya, la'akari da yankin da kasar take da kuma yanayi da ake samu na sanyi da daddare, da iska mai kura da kuma zafi.

Masana dai sun alakanta ta'azzara cutar da karancin tsaftar jiki da na muhalli da yawan al'umma da kuma canfi.

Gwammnatin Nijeriya dai ta tura ayarin likitoci masu binciken musababbin barkewar cututtuka da allurar ragakafi zuwa yankunan da cutar ta bulla domin dakile yaduwarta.

Rigakafi dai, shi ne muhimmiyar hanya ta takaita cutar, inda tuni cikin makon da ya gabata, aka fara bada allurar rigakafin tare da kan al'umma game da cutar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China