in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 15 sun mutu a sakamakon harin saman da sojojin kawanen kasa da kasa suka kai a Syria
2017-04-09 13:51:25 cri
Bisa labarin da kafofin watsa labaru na kasar Syria suka bayar, an ce, kawancen kasa da kasa na yaki da kungiyar IS da kasar Amurka ke jagoranta ya kai harin sama ga wani kauye dake jihar Al-Raqqah ta arewacin kasar Syria, wanda ya haddasa mutuwar mutane a kalla 15.

Kamfanin dillancin labaru na kasar Syria ya rawaito cewa, mutanen da suka mutu sun hada da kananan yara 3, kana harin saman ya haddasa raunatar mutane da dama, watakila yawan mutane da za su mutu zai karu. Bugu da kari an lalata gidajen fararen hula da dama a sakamakon harin saman.

Bisa labarin da kafofin watsa labaru suka bayar, an ce, kawancen kasa da kasa ya kai hare-haren sama a wata makaranta da wani masallaci da aka tsugunar da wadanda suka rasa gidajen su a jihar Al-Raqqah a watan da ya gabata, wadanda suka haddasa mutuwar mutane 77.

A watan Satumban shekarar 2014, kasar Amurka da sauran kasashe suka kafa kawancen kasa da kasa don kai hare-hare ta sama ga kungiyar IS dake kasar Syria da Iraki. A ganin gwamnatin kasar Syria, kawancen ya yi aikin ba tare da samun izni daga kwamitin sulhun MDD ba, kana ta zargi kawancen da kaiwa hare-hare ta sama wadanda suka haddasa mutuwa da raunatar fararen hula da dama. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China