in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mai shiga tsakani na AU ya fara yin taruka a Khartoum gabanin tattaunawar zaman lafiya
2017-04-07 09:29:27 cri
Babban mai shiga tsakani na kungiyar tarayyar Afrika AU Thabo Mbeki, ya fara gudanar da wasu taruka tun a jiya Alhamis gabanin fara sabon zagaye na tattaunawar sulhu tsakanin gwamnatin Sudan da 'yan tawayen SPLM arewaci da kuma mayakan yankin Darfur.

Mbeki, wanda shi ne shugaban tawagar aiwatar da shirin zaman lafiya na tarayyar Afrika a kasar Sudan wato AUHIP, ya fara ganawar ne da Ibrahim Mahmoud Hamid, mataimakin na musamman ga shugaban kasar Sudan kuma shugaban tagawar gwamnati don tattaunawar sulhu,

Bayan kammala tattaunawar, Hamid ya shedawa taron manema labarai cewa, an amince cewar AUHIP za ta ci gaba da daukar matakai wadanda za su tattabar da zaman lafiya a Sudan, kuma za'a shigar da kungiyoyin 'yan tawayen kasar cikin shirin tattaunawar sulhu na kasar.

Jami'in gwamnatin ta Sudan ya jaddada cewa, gwamnatin kasar a shirye take da amince da maido da tattaunawar sulhu tskaninta da 'yan tawayen na SPLM arewaci da masu dauke da makamai na yankin Darfur.

Mbeki ya ce a halin yanzu suna dakon martani daga bangaren kungiyoyin 'yan tawayen kasar domin sanya lokacin ci gaba da tattaunawar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China